Thursday, 2 August 2018

ALLAH SARKI KASATA NAJERIYA...

1.On 2nd April, 1972. Nigeria changed from right hand drive to the letf hand drive.

2. The first women to buy a car in Nigeria was Mrs. Efunroye Tinubu.

3. In 1958 Nigeria flag was designed by Taiwo Akinwumi a Nigeria Student in London as at that time.

4. In 12th Dec. 1991 the seat of the Federal Government was moved from Lagos to Abuja.

5. In 1st Oct. 1979 Alh. Shehu Shagri become first Excutive president.

6. In 1925 the first landing Aerplane in Nigeria took place in Kano.

7. In 1956 Queen Elizabeth visited Nigeria.
8. In 1958 Central Bank of Nigeria was opened for bisinedd.

9. In 1953 the first discovey of  Oil came up.
10. In 1926 Daily Time Newspaper was established.

11. In 1st Jan. 1973 Nigeria changed into metric system of currency (Naira and Kobo).
12. In 1970 Niger Dam (Kanji Dam) was opened and it cost 180 million.

13. In 1955 Chief Obafemi Awolowo introdiced primary education in old western region.
14. In 1923 the first election was held in Nigeria.

15. In 27th 1967 Gen. Yakubu Gowon divided Nigeria into 12 state raised from the former 4 region stricture.

16. The first woman pilot in was Chinyere Anayuchea.

17. The firs woman to drivef a car was Mrs. Funmilayo Ransome Kuti.

18. In 1914  Nigeria named a Nigeria.

19. In 1805 Mungo Park died at New Buss in River Niger.

20. In 3rd Feb. 976 Gen. Murtala Ramat Muhammad created 7 more state bringing up the state in Nigeria from 12

Monday, 11 June 2018

UNGUWAR BAYI A HADEJA

Wani Matambayi ya aiko min da tambayar yana son sanin, a ina Unguwar Bayi ta samo suna, da kuma su wanene mazauna unguwar.

Amsar wannan tambaya ita ce:

Ma’anar Bayi dai shine unguwar da take Ƙofar Baya. Anan ana nufin bayan Fadar Sarki. Ana sane da cewa ƙofofin fadar Mai Martaba Sarkin Hadeja guda biyu ne. Farko ita ce babbar ƙofar da ke gaban fadar a fuskar Yamma, ko kuma Ƙofar Fada a taƙaice. Ita wannan ƙofa, a shekarun baya kafin a rushe ta a gina ta zamani, ana kiranta Mai Tsatstsewa.

Ƙofa ta biyu ita ce wannan ƙofa ta baya, da ke fuskar Gabas, wadda aka fi sani da Kofar Ruhogo (babban rumbun aje kayan abincin Sarki).

A garuruwan Katsina da Zaria ma, haka waɗannan unguwanni suka samo suna. Saidai a Katsina ana kiran wannan unguwa ne da sunan Kofar Bai, a Zaria kuma ana kiranta da Ƙwar Bai. Karin harshe na Haɗejanci (Haɗeja dialect) yasa ake cewa Bayi anan Haɗeja. Kamar yadda wasu suke cewa Sarkin Bayi, a maimakon Sarkin Bai, duk asalin guda ne.

Abu na biyu kuma dangane da batun su wanene mazauna wannan unguwa ta Bayi? Amsar ita ce: akasarin mazauna wannan unguwa mahukuntan Gari da mashawartan Sarki ne, anan gidajen da yawa daga cikin ‘yan majalisa da hakimai suke.

Za’a iya fahimtar fa’idar hakan akan samarda wurin da zai bada damar tuntuɓa ta gaggawa tsakanin Sarki da manyan hakimansa ko ‘yan majalisa ko mashawartansa. 

Sannan kuma kasancewar gidanjen Hakimai a bayan gidan Sarki ya inganta tsaro ga Fadar domin gidajen hakiman kansu kewaye suke da na maƙarrabansu. Ta haka Fadar ta zama tana da kariya gaba da bayanta. Wannan tunani na magabata ta fuskar tsaro yayi matuƙar tasiri a wancan lokaci na yaƙe-yaƙe, kuma hakan ya bayyana ƙarara a shekarun nan da yanayin tsaro ya taɓarɓare a ƙasar nan.

Daga: Engr. Daudu Abdul'aziz

Wednesday, 6 June 2018

CIROMAN HADEJIA SAMBO

An haifishi a Ranar .../.../1909

Matsayin da yafi zama daidai da na Chiroman Hadejia Sambo a wancan lokaci shine kamar matsayin Secretary na local Government a yanzu, domin shine wanda wuk’a da nama ke hannunsa wajen gudanar da aikin N.A. (in charge of N.A. administration).

Aikinsa na farko bayan ya kamala karatu a ‘Katsina Training College’ a shekarar 1930 shine ‘Temporary Teacher’ a Kano Middle School a wannan shekarar ta 1930.

Ya rike mukamin Headmaster a Hadejia Elementary School daga 1932 zuwa 1941.

An yi masa Sarautar Dan Iya daga 1941 zuwa 1950 sannan ya zama Chiroma daga 1950 zuwa 1958 lokacin da Allah ya karbi ransa. Abin lura anan shine Chiroman ba ritaya daga aiki yayi ba, illa dai ta Allah ce ta kasance (Allah ya jikansa da rahama).

‘Member’ ne na Hadejia N.A. Council, sai kuma Member na ‘Area and Provincial Development Commission’ sannan kuma N.A. Schools Manager

A matakin kasa kuma, ya zama dan Majalisar Jihar Arewa dake Kaduna, bugu da kari kuma yayi dan Majalisar Tarayya a Ikko, sannan kuma yana cikin ‘yan majalisa masu rike da kambu biyu, abin da ake kira a wancan lokacin da suna ‘Regional Joint Council’. Bayan wannan ya zama daya daga cikin mambobi na kwamatin da ake kira ‘Regional Committee of Selection’.

Ya halarci kwas na local government tare dasu Sardauna Ahmadu Bello a kasar ingila a 1947.

Monday, 30 April 2018

SARKIN HADEJIA BUHARI AT KAFUR

..."On hearing the drum-beat Galadiman Kano's army began to flee instead of bridling their horses front they bridled their tails. All was confusion as they attempted to save their lives. No one stood his ground some climbed into trees and were caught in them and killed or enslaved. Then a number of the horses and weapons were collected by the HADEJAWA on that day, enven a woman received her on slave. The capture and enslavement of men continued for three days"

Buhari's men took one thousand horses and killed a son of Sarkin Zaria, three sons of Sarkin Kano, and seventeen sons of the Kano chiefs as well as a grandson of Sultan Aliyu.

Reference:

1. Savana Nomads: (A study of the Wodaabe Pastoral Fulani of Western Barno Province, Northern Region, Nigeria). London: Oxford University Press, 1959

2. Hajj Sa'id, (History of Sokoto)

3. Glenny, (History of Certain Emirate)

4. The Sokoto Caliphate, (London longmam Green)

Saturday, 28 April 2018

The popular ranking of gainful occupations practice in Hadejia in 1900. Were significant source of household income. The 22 occupation are as follows:-

1. Long-distance traders
2. Pettt Traders
3. Cattlemen
4. Buchers
5. Sewers (Clothing)
6. Spinners (Cotton)
7. Blacksmiths
8. Builders
8. Dyers
9. Brokers
10. Food Sellers
11. Barber/Doctors
12. Muslim Necromancers
13. Goldsmiths
14. Leather Workers
15. Praise Singers
16. Potters
17. Islamic Scholars
18. Qur'anic Clerics
19. Fishermen
20. Ferrymenn
21. Weavers (Clothing)
22. Hunters

Thursday, 8 March 2018

SARKIN JAUJE TUKUR WADDA YAYI SHAHADA A YAƘIN HADEJIA DA TURAWA YANA YIWA SARKIN HADEJIA MUHAMMADU WAƘA YANA CEWA...

1. Muhammadu ne Toron Giwa, Na Sambo ka wuce raini Sarki.

2. Na Amadu Angon Kura, Kana Ɗaka ke Gayya na Garba da fitarka a watse ɗai ɗai, Na Abdu Hurdi ɗagogon Bannu, Jitau na Jarma abin ƙauna.

3. Bisa ga lumana Sarki, an ƙira ka Katagum ka je, haka ka je Sharfar ka zo, In ko babu lumana Hurdi, ƙofa tasa ma bai je ba bare su Bariki can mai nisa.

4. Ka lura Muhammadu na Garba, Ga Sarkin  Malle sai yawo take, Ga Sarkin Bidda da ma Sarkin Sudan, na Kwantagora ka duba, duka sun gudu don tsoro.

5. Uban Kabo Mamman ɗa, da gudun sa a goranta masa, kuma ko kowa a kama shi, Na Sambo gara kisa take, ƙi gudu gara shahada ta fi.

6. Da wulakanci ɗibgau, Shahada ta fi Muhamman, Da ka bisu a Tozarta ka, jama'ar ka su ɗai-ɗaice, na Amadu gara a gwabza ya fi.

7. Da dai na baya su goranta mana, Ace mun kasa har kai, ko ka gudu don tsoron wani, Ai gara mu ƙare duk, Da mu bar baya da Gorin banza.

8. Sa gudu baya wargi, Haka baya son mai wargi, kai ne Buhari tuna sosai, Da ka bi su a kama ka, Muhammadu gara ka kwana Kushewa.

9.

10.

Ismaila A Sabo

Thursday, 1 March 2018

HARAJI A HADEJIA A LOKACIN TURAWAN MULKIN MALLAKA

Wani muhimmin al'amari a mulkin Turawa ya danganci tarawa da karban kudaden shiga da za'ayi amfani dasu wajen tafiyar da al'amuran mulki. Turawan mulki sun lura da cewa hanyoyin da masarautar Hadejiya take amfani dasu a da wajen tara kudaden shiga ba su gamsar da suba. Turawan mulki sun so mutane kalilan su kasance masu gudanar da wannan aikin, wadanda cikin sauki za'a rinka kulawa da su da kuma dora musu nauyin duk abinda ya fara na almubazzaranci da kudaden jama'a. Ta hakane kawai za'a iya kiyaye koda da oda na wannan aikin. Daga nan ne Turawa suka kawo wani tsari sabo na saukaka hanyoyin tara kudaden shiga. A wannan sabin tsarin, a wannan kamar yadda aka bayyana a baya kadan, an nemi hakimai su koma garuruwansu da zama su sa ido a kan harkikin gurarensu. Ta haka aka rushe matsayin Jakadu a kaikaice.

To a, wannan tsarin mai unguwa zai karbi harajin jama'arsa zai tattara wadannan kudade ya kai wa hakiminsa kai tsaye, daga nan shi kuma zai dauka ya kai wa Sarki.

Ikon tarawa da binciken kudaden shiga kuma na Resdan ne ko kuma wakilansa, amma duk da haka wannan ikon an bawa hakimai shi zuwa dan wani lokaci. An cigaba da karban ire-iren haraji a 1906 in banda wasu kadan kamar harajin sana'a.

Haka kuma an kirkiro wasu nau'o'in haraji, Misali a 1914 aka shigo da kudin su inda aka dirawa masunta su dinga biyan wasu 'yan kudi gwargwadon kimar kifin da suka kama ko kimanin kayan kamun kifin da suke amfani da su. Domin haka masunta masu amfani da koma za su biya kudi kasa dana masunta masu amfani da taru domin nasu yafi girma kuma yafi kami kifi da daya.

Haka kuma an shigo da harajin magidanta da kudin gona da ake karba gwargwadon fadi da tsayin gona . Daga nan kuma Turawan mulkin mallaka suka suke Zakka da Jizya wadanda ake karba a lokacin daular masu jihadi ta Sakkwato. Ta haka ne Turawan mulki suka gwama tsakanin kudaden shiga da ake karba kafin 1906 da wadanda suka shigo da su sababbi inda tsarin ya fara aiki a wajajen 1918.

Daga wannan lokaci ne aka fara buga haraji ga mutanan kasa inda aka aza wa mutum daya magidanci Sule Biyar, shi kuma matashi wanda ya kai farfi Sule Uku. Ga kuma Jangali inda aka sa wa kowace saniya daya Sule daya da 'yan kai.

Da farko harajin da aka tara ana rabshi kashi biyu, "kashi daya za a turawa Gwamnatin Ingila" sauran kashi daya za a barwa hukumar cikin gida domin biyan bukatunta na mulki. Daga baya kuma aka yankawa ma'aikatan N.A albashi a kowana karshen wata.

An fara sabon tsarin ajiye kudi a Baitul-Mali a Hadejia da Katagum a shekarar 1909. Turaki shi ne ya fara zama ma'ajin farko na Baitul-Malin Hadejia, "amma a shekarar 1911 an sami wani sabani ya faru tsakaninsa da Sarkin Hadejia Abdul'kadir da Turaki Munkaila akan yadda za a kashe kudaden da ake tarawa. To tun daga wannan lokaci Sarki ya ci gaba da kula da Baitul-Mali da kansa har zuwa lokacin da aka nada wani amintaccen Sarki sabon Ma'aji.

Har wa yau kuma a shekarar 1915 an sake samun wani saban tsari a Hadejia a wannan lokacin an kirkiro wani lardi daga masarautar Katagum da Gumel da kuma Hadejia wannan lardi an fara ajiye hedikwatarsa a Gumel, amma a shekarar 1916 sai aka mayar da ita izuwa Hadejia. Daga nan kuma aka sake daddatsa gundomumin Masarautar Hadejia zuwa guda tara a karkashin ikon Rasdan W.F Gower. Wadannan sababbin gundumomi sun hada da:-
1. Gundumar Birniwa  Sarkin Arewa
2. Gundumar Guri  Ciroma
3. Gundumar Garun Gabas  Mabudi
4. Gundumar Kirikasamma  Sarkin Damawaki
5. Gundumar Kaugama  Madaki
6. Gundumar Auyo  Sarkin Auyo
7. Gundumar Kafin Hausa  Sarkin Bai
8. Gundumar Bulangu Wambai
9. Gundumar Dakido Tafida

Wadannan gundumomi tara 9 suna ci gaba da wanzuwa har zuwa shekarar ta 1926 a lokacin da aka sake zuwa da wani sabon tsari kuma inda lardin Katagum wanda ya hada masarautun  Katagum da Jama'are da Misau aka mayar da shi a cikin lardin Bauchi. Shi kuma lardin Katsina ya koma cikin lardin Zariya, Hadejia da Gumel da Daura da Kazaure aka sake hada su a wani sabon lardin Arewa aka yi masa hedikwata a Hadejia.
Har ila yau kuma wadannan gundumomi tara 9 an sake rage yawansu aka mayar dasu bakwai 7 gasu kamar haka:-
1. Kafin Hausa
2. Malam Madoei
3. Bulangu
4. Guri
5. Auyo
6. Kirikasamma
7. Birniwa

Wannan shi ne tsarin na karshe wanda Turawan Mulkin Mallaka suka tashi suka bari a dai-dai a karshen 1959.

Abin tambaya a nan shi ne yaya jama'ar kasa suka karbi wadannan canje-canje?
Hakika jama'a basu yi na'an da wadannan tsare-tsare ba, a wani wurin ma suna nuna fushinsu. Wadannan tsare-tsare bisa yawanci sun kara wa talakawa ne nauyi ta hanyar dora musu harajin Kai da na sana'o'i, ga kuma ayyukan gayya da ake sa suyi a ko da yaushe ba tare da an biya su ba, haka kuma tsare-tsaren sun haifar da rashin cikakkiyar biyayya, Misali a gundumar Gizimawa da Badawa suna biyan harajinsu ta hanyar Sarkin Bade, amma a sabon tsarin Turawa sai a suka dora musu Ciroma. Wannan ya kawo rashin nutsuwa ga mutanen Bade domin wani bangare na Gizimawa ma sai da suka bijire wa biyan haraji. Daga nan Turawan Mulkin Mallaka suka kama shugabanin wada suka ki biya aka sa su a kuekuku, daga baya aka sasanta kowa ya biya nauyin da aka dora masa. Amma duk da haka wasu sun ki biya, a saka makon haka ne sukayi kaura zuwa Gumel. SULEIMAN GINSAU

MADOGARA

Heussler, R. (1968) The Biritish in Northern Nigeria. London: Oxford University Press.

Gower, W.F. (1921) Gazetteers of Kano Province. London: Frank Cass

Hiskett, M.A (1975) Two Verse Account of Hadejia History a cikin History of Hausa Islamic Verse.

Wakili H. (2005) Turawa a Kasat Hadejia. Benchmark Publishers Ltd.

Monday, 22 January 2018

HAKIMAN HADEJIA SU GOMA SHA HUDU (14) NE A 1972.

Hakiman kasar Hadejia a 1972 gaba dayan su goma sha hudu (14) ne, bakwai (7) a cikin gari, guda Takwas  (8) Masu k'asa

- HAKIMAI 'YAN MAJALISA

1. GALADIMA ALH. YUSUFU

2. DAN IYA ABDULKADIR MAIDUGU

3. MADAKI MUHAMMADU GAUYAMA

4. TURAKI ALH. ADAMU SADAU

5. DAN BURAN MUHAMMADU HURDI

6. TAFIDAN HADEJIA ADULKADIR MAIGARI

7. DAN LAWAN ALH. ABUBAKAR

- HAKIMAI MASU K'ASA

1. SARKIN AREWA ALH. USMAN ABUBAKAR (BIRNIWA)

2. SARKIN DAWAKI ALH. DAUDA USMAN (KIRI-KASAMMA)

3. SARKIN BAI MUHAMMADU BASHARI (GURI)

4. DOKAJI SALE KULIYA (MALAM-MADORI)

5.  CHIROMA MUHAMMADU ABBAS (KAFIN-HAUSA)

7. ALH. MUHAMMADU UMARU SARKIN AUYO (AUYO)

8. WAMBAI MUHAMMADU (BULANGU)